Home General Jami’an tsaro sun dakile haring ‘yan bindiga a Jihar Katsina

Jami’an tsaro sun dakile haring ‘yan bindiga a Jihar Katsina

Jami’an tsaro a jihar Katsina sun samu nasarar daƙile yunƙurin ƴanbindiga na kai hari a ƙaramar hukumar Ɗanmusa da ke jiyar, wadda take arewa maso yammacin ƙasar.

Kakakin rundunar ƴansandan jihar Katsina, DSP Abubakar Sadiq ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, inda ya ce jami’an tsaron sun samu nasarar ne a ranar Asabar.

“A ranar 15 ga watan Maris ce jami’an tsaron farin kaya suka samu bayanan sirri cewa ƴanbindiga suna taruwa a tsaunin Maijele da ke ƙaramar hukumar Ɗanmusa domin kai hari a ƙauyen Ɗan Takuri.

“Da samun labarin ne jami’an tsaron haɗin gwiwa na ƴansanda da askawaran Katsina suka kai ɗauki, inda aka yi musayar wuta tsakanin ƴanbindigar da jami’an tsaro.”

Ya ce a ƙarshe dai jami’an tsaron sun samu nasarar fatattakar ƴanbindigar, tare da kashe ɗaya daga cikinsu, sannan aka ƙwato wasu makamai da ƙwayoyi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp