A Jamhuriyar Nijar gwamnatin kasar ta bayyana Hausa a matsayin harshen da za a rinka amfani da shi a kasar yayin da sauran harsuna ta ayyanasu a matsayin na magana.
Kazalika an kuma bayyana harshen Ingilishi da Faransanci a matsayin harsunan aiki.
To sai dai kuma ba dukkanin ‘yan kasar ne ke maraba da wannan mataki ba.
An kiyasta cewa akwai mutum miliyan 18 da ke jin harshen Hausa a Jamhuriyar Nijar, abin da ake ganin wannan ne ya sanya gwamnatin kasar ta ayyana shi a matsayin harshen da za a rinka amfani da shi a kasar.
To sai dai kuma ba dukkanin ‘yan kasar ne wannan mataki ya yi wa dadi ba, inda wasu ke cewa ya kamata a yi nazari sosai a kai.
Harshen Hausa shi ne ke matsayin na uku a Afirka inda kasashe da dama a Afirka a ke samun masu jin harshen.
Akwai dai masu jin harshen Hausa a kasashe kamar Najeriya da Nijar da Kamaru da Ghana da Chadi da Sudan da Benin da Togo da Gabon da kuma Burkina Faso.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 15 hours 12 minutes 18 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 16 hours 53 minutes 43 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com