Home General Ƙasashen AES sun yi wa jakadunsu a Aljeriya ƙiranye

Ƙasashen AES sun yi wa jakadunsu a Aljeriya ƙiranye

Ƙasashen kungiyar  AES sun yi wa jakadunsu da ke Aljeriya kiranye a jiya lahadi ,bayan Mali ta zargi kasar da ƙaƙƙabo wani jirgin yakinta mara matuki a kusa da Tinzaouatene.

A cikin  daren 31 ga watan Maris da ya gabata wayewa safiyar 1 ga watan nan na Afrilu Aljeriya ta sanar da ƙaƙƙabo wani jirgi mara matuki mallakin sojojin Mali da ta zarga da keta sararin samaniyarta a kusa da Tinzaouatene da ke kan iyakar kasashen biyu.

A wata sanarwa da suka fitar a jiya lahadi kasashen AES wato Mali,Nijar da Burkina Faso sun bayyana bakin cikinsu da afkuwa lamarin tareda jaddada cewa kai hari kan daya daga cikin kasashen tamkar kaiwa baki dayan kungiyar hari ne.

Ministan harakokin wajen Mali Abdoulaye Diop ya bayyana lamarin da mai matukar muni ,lura da yadda tarwatsa jirgin ya hana dakarun kasar  cimma burinsu na ƙaƙƙabe wani gungun ‘yan ta’adda da ke tsara kai hare-hare kan kasashen AES.

Ƙasashen na  AES wato Mali da Nijar da kuma Burkina Faso sun zargi Aljeriya da taƙalar fada sanan sun sha alwashin kai kararta a gaban hukumomin ƙasa da ƙasa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp