Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta na hadin gwiwar Operation Fasan Yamma sun kashe ‘yan ta’adda 10 a jihar Zamfara.
Rundunar ta ce sojojin sun kashe ƴan ta’addan ne a cikin wani mummunan farmaki da suka kai a wuraren da ‘yan ta’addan ke zama a Mai Tashi da Dan Jigba a ƙaramar hukumar Gusau, da kuma Munhaye a ƙaramar hukumar Tsafe a Zamfara, a jiya, 9 ga Yunin 2025.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafin sada zumuntarta na X.
A yayin wannan aiki, an ƙwato makamai da dama da alburusai.
Sannan kuma rundunar ta ce an ƙona babura guda 5 da ‘yan ta’addan ke amfani da su a wuraren da aka kai farmakin.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1461 days 21 hours 19 minutes 33 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1443 days 23 hours 58 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com