Home General Sojojin Najeriya sun kashe ƴan ta’adda 10 a Zamfara

Sojojin Najeriya sun kashe ƴan ta’adda 10 a Zamfara

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta na hadin gwiwar Operation Fasan Yamma sun kashe ‘yan ta’adda 10 a jihar Zamfara.

Rundunar ta ce sojojin sun kashe ƴan ta’addan ne a cikin wani mummunan farmaki da suka kai a wuraren da ‘yan ta’addan ke zama a Mai Tashi da Dan Jigba a ƙaramar hukumar Gusau, da kuma Munhaye a ƙaramar hukumar Tsafe a Zamfara, a jiya, 9 ga Yunin 2025.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafin sada zumuntarta na X.

A yayin wannan aiki, an ƙwato makamai da dama da alburusai.

Sannan kuma rundunar ta ce an ƙona babura guda 5 da ‘yan ta’addan ke amfani da su a wuraren da aka kai farmakin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp