Home General Nan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur...

Nan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur na Najeriya – Dangote

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote Alhaji Aliko Dangote, ya ce nan bada jimawa ba al’umma Najeriya za su ga gagarumin sauyi a ɓangaren man fetur ɗin ƙasar.

Dangote ya bayyana hakan ne a lokacin da ya ke ganawa da manema labarai, a lokacin da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya ziyarci matatar mansa ta dala biliyan 20, da ke yankin Lekki a jihar Lagos.

Ya ce sauyin da al’umma za su gani a yanzu, ba wai na rage farashin man ba ne, wanda zai sauya baki ɗaya yadda ake gudanar da harkokin mai ne a ƙasar.

A yanzu da shugaban ƙasa ya ziyarcemu, kuma ya bamu ƙarin makamashi, ina mai sheda muku cewa nan bada jimawa ba za ku ji daga garemu, kuma zai kasance sauyi ne a ɓangaren mai baki ɗaya a ƙasar, ba wai kawai rage farashinsa ba ka ɗai.

A watan Oktoban bara ne dai matatar man Dangote ta fara saida man fetur, lamarin da ya kawo saukar farashinsa a Najeriya.

To sai dai dillalan man fetur a Najeriya, na ganin ya kamata matatar Dangoten ta rinƙa saida lita ɗaya ƙasa da Naira ɗari 8, la’akari da cewar ana sayar wa kamfanin ne da ɗanyen mai a kuɗin Naira maimakon dalar Amurka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp