Home General Nan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur...

Nan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur na Najeriya – Dangote

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote Alhaji Aliko Dangote, ya ce nan bada jimawa ba al’umma Najeriya za su ga gagarumin sauyi a ɓangaren man fetur ɗin ƙasar.

Dangote ya bayyana hakan ne a lokacin da ya ke ganawa da manema labarai, a lokacin da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya ziyarci matatar mansa ta dala biliyan 20, da ke yankin Lekki a jihar Lagos.

Ya ce sauyin da al’umma za su gani a yanzu, ba wai na rage farashin man ba ne, wanda zai sauya baki ɗaya yadda ake gudanar da harkokin mai ne a ƙasar.

A yanzu da shugaban ƙasa ya ziyarcemu, kuma ya bamu ƙarin makamashi, ina mai sheda muku cewa nan bada jimawa ba za ku ji daga garemu, kuma zai kasance sauyi ne a ɓangaren mai baki ɗaya a ƙasar, ba wai kawai rage farashinsa ba ka ɗai.

A watan Oktoban bara ne dai matatar man Dangote ta fara saida man fetur, lamarin da ya kawo saukar farashinsa a Najeriya.

To sai dai dillalan man fetur a Najeriya, na ganin ya kamata matatar Dangoten ta rinƙa saida lita ɗaya ƙasa da Naira ɗari 8, la’akari da cewar ana sayar wa kamfanin ne da ɗanyen mai a kuɗin Naira maimakon dalar Amurka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp