Home General An samu tashin gobara a masaukin alhazan Najeriya a Shari Mansur

An samu tashin gobara a masaukin alhazan Najeriya a Shari Mansur

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin gobara a ɗaya daga cikin otal ɗin da alhazan ƙasar ke zaune a ciki a Shari Mansur da ke birnin Makka.

Wata sanarwa da hukumar ta fitar yau Asabar, ta ce otal ɗin ya kasance yana ɗaukar mahajjata 484, sai dai ba a samu asarar rayuka ba saboda dukkan alhazan na Mina.

Hukumar agajin gaggawa ta Saudiyya da hukumar gudanarwar otal ɗin ne suka yi ƙoƙarin kashe gobarar.

Shugaban hukumar Alhazai ta Najeriya, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya bayar da umarnin sauyawa alhazan wurin zama lokacin da kai ziyara wurin.

Ya jajantawa waɗanda gobarar ta shafa tare ɗaukar alwashin taimaka musu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp