Home General An samu tashin gobara a masaukin alhazan Najeriya a Shari Mansur

An samu tashin gobara a masaukin alhazan Najeriya a Shari Mansur

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin gobara a ɗaya daga cikin otal ɗin da alhazan ƙasar ke zaune a ciki a Shari Mansur da ke birnin Makka.

Wata sanarwa da hukumar ta fitar yau Asabar, ta ce otal ɗin ya kasance yana ɗaukar mahajjata 484, sai dai ba a samu asarar rayuka ba saboda dukkan alhazan na Mina.

Hukumar agajin gaggawa ta Saudiyya da hukumar gudanarwar otal ɗin ne suka yi ƙoƙarin kashe gobarar.

Shugaban hukumar Alhazai ta Najeriya, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya bayar da umarnin sauyawa alhazan wurin zama lokacin da kai ziyara wurin.

Ya jajantawa waɗanda gobarar ta shafa tare ɗaukar alwashin taimaka musu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp