Home AFIRKA yadda mahara suka hallaka sojojin Nijar sama da 30

yadda mahara suka hallaka sojojin Nijar sama da 30

Aƙalla sojoji 34 ne wasu mahara da ake zargin masu ikirarin jihadi sun kashe a Jamhuriyar Nijar, sannan suka jikkata wasu mutum 14.

An kai harin ne a garin Banibangou, wanda ke kan iyakar Nijar da Mali da Burkina Faso, inda ake tunanin akwai mahara masu ikirarin jihadi da suke da alaƙa da ƙungiyar Al Qaeda.

Ma’aikatar tsaron Nijar ta yi Allah-wadai da harin, wanda ta bayyana da “na rashin hankali,”.

Ma’aikatar ta ce “an kai harin ne a ranar Alhamis 19 ga watan Yuni. Wanda hari ne na dabbanci da aka kai a garin Banibangou, wanda wasu mahara waɗanda baƙi ne suka kai a babura sama 200,” kamar yadda ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar.

Sanarwar ta ƙara da cewa sojojin ƙasar sun kashe “gomman maharan,” a lokacin da suke musayar wuta, sannan ta tura ƙarin jami’a zuwa yankin.

A yanzu haka dai Nijar da Burkina Faso da Mali suna ƙarƙashin mulkin soji ne waɗanda suka ƙwace mulki bayan hamɓarar da zaɓaɓɓun shugabannin ƙasar, sannan suka kafa ƙawancen tsaro.

Sai dai duk da ƙawancen, har yanzu ƙasashen yankin suna fama da rikice-rikice a ƴan watannin da ake ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp