Home General Mutane 5 sun gamu da ajalinsu sakamakon fashewar wani abu a Kano

Mutane 5 sun gamu da ajalinsu sakamakon fashewar wani abu a Kano

Aƙalla mutane biyar aka tabbatar  sun mutu, kana wasu 15 suka jikkata sakamakon fashewar wani abu da ake zargin bam ne a Jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Rundunar ƴansandan jihar, ta bakin kwamishinanta, Ibrahim Adamu Bakori, wadda ta tabbatar da aukuwar lamarin, ta ce ya faru ne akan bypass na Mariri dake yammacin birnin Kano.

Rahotanni sun ce jami’an ƴansanda da na hukumar agajin gaggawa sun garzayar wurin da aka samu fashewar domin kai ɗauki, a yayin da lamarin ya haddasa ruɗani da firgici a zukatan al’ummar yankin.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya ce fashewar na iya kasancewa bam ɗin da sojoji suke jigilarsa ne wanda aka yi sakaci ya fashe.

Binciken farko-farko ya nuna cewa abin fashewar na cikin wata babbar mota ce, wadda ta ɗauko kaya, mallakain wasu masu sana’ar gwangwan, kuma take kan hanyar zuwa Jihar Yobe.

Rundunar ƴansandan Kanon ta ce ta gani wasu ƙakkrin abubuwan fashewa da ba su kai ga tashi ba a inda lamarin ya faru, kuma  tana  cigaba da bincike akan yadda aka samo su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp