Home Labarai Yadda Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Yadda Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami’an tsaro a Nigeria sun kama Mai Wasan barkwancinan a shafukan sada zumunta Dr. Bello Habib Galadanci wanda aka fi Sani da Danbello.

Danbello dai ya jima ya yin wasanni barkwanci inda a ciki yake nuna yadda Shugabanni a Nijeriya suka Gaza yiwa talakawan Kasar abubuwan da suka dace.

An dai kama Danbello ne a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano dake Kano , Jim kadan bayan saukarsa daga jirgin sama .

Dama dai Danbello yana zaune ne a Kasar China inda daga chan yake yin duk abun da yake yi .

Ana zargin Jami’an tsaron da suka kama Danbellon sun zo ne daga Abuja.

Sai dai duk da cewa ba a bayyana dililin kama Danbello ba, Amma mintoci kadan bayan kama shin kuma aka sake shi .

A wata hirarsa da manema labarai Danbello ya ce ” Bayan sakkowarmu daga jirgi sai wasu mutane masu kama da Jami’an tsaro suka karbi Fasfo dina da sauran takarduna , kuma suka ce In shiga wata mota”.

” Ana haka sai ga Barr. Abba Hakima nan sai akai Dan yi waya sannan akai dogon turanci bayan awa daya sai suka sallameni, Amma dama ban yi mamakin kamani ba, don dama da Shirin hakan na zo.

Tuni dai Danbello yana cikin Iyalansa bayan sakinsa da Jami’an tsaron suka yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp