Home Labarai Buhari mutum ne mai gaskiya da kishin ƙasa – IBB

Buhari mutum ne mai gaskiya da kishin ƙasa – IBB

Tsohon shugaban mulkin soji a Najeriya Janar Ibrahim Babangida ya miƙa ta’aziyarsa bisa rasuwar tsohon shugaban ƙasar, Muhammadu Buhari inda ya bayyana shi da mutum mai kyawawan halaye, kuma mai kishin ƙasa.

IBB wanda ya hamɓarar da Buhari daga mulkin soji a ranar 27 ga watan Agustan 1985, ya bayyana shi a matsayin mutumin da ko bayan barinsa mulki, ya cigaba da kasance abin koyi ga mutane da dama kuma abin misali.

Ya kuma tuna lokacin da ya fara haɗuwa da marigayi Buhari a shekarar 1962 a lokacin da suka shiga makarantar horar da sojoji da ke Kaduna.

“Tun a lokacin Muhammadu Buhari mutum ne na daban, bai cika magana ba, amma yana da jajircewa, kuma mutum ne mai bin ƙa’ida kuma mai sauƙin kai, mai tsananin kishin ƙasa ne da sadaukar da kai ga Najeriya. A cikin shekarun, mun kasance tare cikin wahala da daɗi da jarabawa da kuma cin nasara da rashinsa.”

Babangida ya ce duk da shi da Buhari sukan saɓa kan wasu abubuwa, kamar yadda a kan samu tsakanin ƴanuwa, “amma ko kaɗan ban taɓa kokwanto game da gaskiyarsa da kishin ƙasa ba.

”Bayan aiki kuma na san shi a matsayin mutum mai addini wanda kuma ke tafiyar da rayuwarsa cikin tawali’u.” in ji tsohon shugaban mulkin sojin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp