Fitaccen ɗan siyasa kuma tsohon gogaggen ɗanjaridar nan na Najeriya, Dele Momodu ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar PDP zuwa sabuwar haɗakar ADC ta ‘yan hamayya.
Momodu – wanda ya taɓa tsayawa takarar shugaban ƙasar – ya ce ya ɗauki matakin ne saboda yadda wasu da ya kira ”masu yaƙi da dimokraɗiyya” suka hana jam’iyyar numfashi.
Read Also:
Cikin wasiƙar ficewar tasa da ya aike wa shugaban jam’iyyar na mazaɓarsa ta Ihievbe a ƙaramar hukumar Owan ta Gabas, ranar Alhamis 17 ga watan Yuli, fitaccen ɗansiyasar ya ce dole ce ta sa ya ɗauki matakin domin maido da martabar dimokraɗiyya.
“Dalilina a bayyane yake, wasu masu yaƙi da dimokraɗiyya sun maƙure jam’iyyar daga ciki da wajen jam’iyyar”, kamar yadda wani sashe na wasiƙar ya nuna.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1491 days 2 hours 55 minutes 1 second,
Baptist School Students, Kaduna
1473 days 4 hours 36 minutes 26 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com