Home Labarai EFCC ta kama ƴan damfara ta intanet 25 a Jami’ar Bayero dake...

EFCC ta kama ƴan damfara ta intanet 25 a Jami’ar Bayero dake Kano

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Najeriya (EFCC) ta kama wasu mutum 25 da ake zargi da aikata damfara ta intanet a wani samame da ta kai a harabar jami’ar Bayero da ke Kano.

Hukumar ta ce jami’anta sun gudanar da samamen ne bisa sahihan bayanan sirri da suka samu da ke nuna cewa mutanen na da hannu a ayyukan damfara ta intanet da kuma satar bayanan mutane.

Hukumar ce ta sanar da hakan a shafin sada zumuntanta na X. inda ta ce dukkan waɗanda aka kama dalibai ne na jami’ar, kuma an gano wayoyi da kwamfutoci da mota kirar Honda Accord a hannunsu.

Kayan da aka kwato daga wurin sun haɗa da wayoyin salula, kwamfutoci, na’urorin haɗi da mota kirar Honda Accord.

EFCC ta ce an kama su ne bayan makonni ana sa ido a kansu kuma za a gurfanar da su a kotu da zarar an kammala bincike.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp