Home General Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da rasuwar Sarkin Gusau na jihar

Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da rasuwar Sarkin Gusau na jihar

Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da mutuwar sarki na 16 a jerin sakarakunan Gusau  mai Martaba Dr. Ibrahim Bello.

wannan dai na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan Jihar Sulaiman Idris Ya fitar tare da bayyana jimamin Gwamnatin jihar bisa wannan babban rashi.

sanarwar ta kuma bayyana kaduwar gwamnan jihar Dauda lawan, wanda ya  bayyana marigayi sarkin matsayin babban uba kuma shugaba mai kishin ci gaban jihar Zamfara.

“Ina matuƙar alhini da jin labarin rasuwar mahaifinmu, Mai Martaba Sarkin Gusau, Dr. Ibrahim Bello.” in ji sanarwar.

“Ina mika ta’aziyya ta ga majalisar sarakunan jihar da iyalan marigayin da masarautar Gusau da kuma ɗaukacin al’ummar jihar Zamfara.” gwamnan ya cewa.

Sarkin dai ya rasu a ranar Juma’a yana da shekaru 71, bayan fama da doguwar jinya a birnin Abuja, wanda shi ne sarki na 16 a jerin sarakunan Gusau, kuma ya gaji mahaifinsa da ya rasu a ranar 16 ga Maris, 2015.

Marigayin ya shafe shekaru 10 da wasu watanni yana kan karagar mulki. daga bisani sanarwa bayyana cewa za’a yi Jana’iza sa a yau juma a garin Gusua

Daga PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp