Home Labarai Hare-haren ƴan bindiga a jihar Filato na ci gaba da lakume rayuka

Hare-haren ƴan bindiga a jihar Filato na ci gaba da lakume rayuka

Akalla mutum 14 da wani ɗan sanda na MOPOL ne suka mutu a hare-hare biyu da wasu ‘yan bindiga suka kai a ƙaramar hukumar Bokkos da ke Jihar Filato a ranar Alhamis, 24 ga Yuli, 2025.

Rahotanni sun ce an kai ɗaya daga cikin hare-haren ne da misalin ƙarfe 4 na yamma, yayin da mutanen da lamarin ya shafa mafi yawansu daga ƙauyen Chirang ke dawowa daga kasuwar Bokkos zuwa ƙauyen Mangor.

Shugaban masu sa ido kan zaman lafiya na ƙaramar hukumar Bokkos, Kefas Mallai ne ya tabbatar da faruwar lamarin ga jaridar Punch inda ya ce mutane 14 ne suka mutu, yayin da wasu uku kuma suka jikkata.

A cewar Mallai, kafin wannan harin, wasu ‘yan bindiga sun harbe wani ɗan sandan MOPOL a wani shingen bincike da ke hanyar Richa a safiyar ranar.

Shugaban ƙaramar hukumar Bokkos, Amalau Amalau, ya bayyana lamarin a matsayin “taƙaici da ke buƙatar ɗaukar matakin gaggawa,” yana mai cewa an riga an kai gawarwaki da waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Alabo Alfred, bai samu damar bayyana komai ba a lokacin da aka nemi jin ta bakinsa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp