Home General Hadarin jirgin ruwa yayi sanadin mutuwar mutum 6 a jihar Jigawa

Hadarin jirgin ruwa yayi sanadin mutuwar mutum 6 a jihar Jigawa

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa a Arewa Maso yammacin Nijeriya ta tabbatar da mutuwar mutane 7 cikin su har da kananan yara sakamakon hadarin jirgin ruwa a karamar hukumar Taura dake jihar.

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin rundunar SP Shi’isu Lawan Adam, Anipr, ya aikewa PRNigeria a yammacin ranar talata, inda ya ce  rundunar ta nuna bakin cikin ta bisa aukuwar hadarin da ya rutsa da matafiya a kauyen Zangwan Maje dake karamar hukumar ta Taura.

Sanarwa ta ce a ranar 27 ga watan Yunin 2025, rundunar ta sami wani kiran gaggawa da ke cewa a kalla yara 15 dake kan hanyarsu ta dawowa daga gona a Jejin Gunka zuwa kauyen Zangwan Maje jirgin da suke ciki ya kife bisa Ambaliyar ruwa da iska mai karfi da kuma lodin da suka yiwa jirgin ya wuce kima.

Sai dai bayan daukin gaggawa da aka kai musu an sami nasarar kubutar da yara 7 a raye, yayin da aka sami nasarar gano gawarwakin yara 2 dukkanninsu mata, haka nan kuma a safiyar talata an sami nasarar gano gawarwakin yara mata 4.

Tuni dai likitoci suka tabbatar da mutuwar yaran kamar yadda sanarwar ta tabbatar.

Kwamishinan ‘yansandan jihar CP, Dahiru Muhammad, psc, fdc ya mika ta’aziyyarsa ga iyalai da ‘yan uwan wadanda hadarin ya rutsa da su da ma daukacin al’ummar kauyen Zangwan Maje.

Ya kuma yi kira ga mazauna yankin da su kaucewa yin tafiyar dare, tare da gujewa daukar kayan da suka wuce kima, su kuma ringumi yin amfani da rigar ruwa a dukkan lokacin da za su shiga jirgin ruwa.

Daga PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp