Home AFIRKA Zanga-zanga ta barke a sansanin ƴan gudun hijra mafi girma da ke...

Zanga-zanga ta barke a sansanin ƴan gudun hijra mafi girma da ke Kenya

Wasu Rahotannin sun bayyana cewa zanga-zanga ta ɓarke a daya daga cikin manyan sansanonin ‘yan gudun hijira na Kenya a ranar Litinin, inda aka samu rahoton mutuwar mutum ɗaya da jikkatar wasu, bayan watanni da aka shafe ana tankiya saboda katsewar agaji.

Sansanin ‘yan gudun hijira na Kakuma, da ke arewacin Kenya, shine na biyu mafi girma a ƙasar, kuma yana ɗaukar ‘yan gudun hijira kusan 300,000 daga Sudan ta Kudu da Somalia da Uganda da kuma Burundi.

Ƙungiyoyin agaji sun sha fama da tankiya tsawon watanni bayan katse tallafin da Amurka da sauran masu ba da agaji suka yi.

Wata majiya daga ma’aikatar kula da ‘yan gudun hijira ta shaida wa kamfanin dillacin labarai na AFP cewa, Mutum ɗaya ya mutu, kuma wasu jami’an ‘yan sanda biyu sun jikkata, yana mai cewa an samu karuwar matsin lamba kan tsarin tallafin.

Duk da haka, kakakin ‘yan sanda ƙasar Michael Muchiri ya tabbatar da kasancewar jami’an a wajen rikicin amma ya ce babu wanda ya rasa ransa.

Ya ce matakin da gwamnatin Amurka ta ɗauka na katse tallafin USAID ya fara yin tasiri a kan halin da ‘yan gudun hijira ke ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp