Home Labarai Gini kan magudanan ruwa ne ya haifar da Ambaliyar Maiduguri

Gini kan magudanan ruwa ne ya haifar da Ambaliyar Maiduguri

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya NEMA ta ce mamakon ruwan sama da yin gine-gine kan magunan ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri.

A ranar Laraba ne aka samu rahotonni ambaliya a wasu unguwannin birnin Maiduguri da yankin ƙaramar hukumar Jere sakamakon ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da aka shafe tsawo sa’a uku ana tafkawa a birnin.

Cikin wata sanarwa da shugaban hukumar NEMA, Zubaida Umar ta wallafa a shafinta na Facebook ta danganta ambaliyar da rashin bin tsarin gine-gine.

”ambaliyar na da alaƙa da mamakon ruwan sama da aka samu a birnin da kuma rashin kula da kwalbatoci da yin gine-gine kan hanyoyin da ruwa ke bi”, in ji shugabar ta NEMA.

Hukumar ta NEMA ta ce jami’anta tare da haɗin gwiwar sauran hukumomi sun taimaka wajen ceto mutanen da ambaliyar ta rutsa da su tare da rage illar ambaliyar.

Ambaliyar na zuwa ne ƙasa da shekara guda bayan wata mummunar ambaliyar da ta auka wa yankin, wadda ta yi sanadiyyar raba fiye da mutum miliyan guda da muhallansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp