Home Labarai KACHMA ta yabawa KAROTA bisa inganta lafiyar Jami’anta

KACHMA ta yabawa KAROTA bisa inganta lafiyar Jami’anta

Hukumar Kula da zirga-zirgar ababawan hawa ta jihar Kano (KAROTA) na shirin yin hadin gwiwa da KACHMA don inganta lafiyar ma’aikatanta

Wannan na cikin wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a  na hukumar Abubakar Ibrahim Sharada ya fitar ya kuma aikewa PRNigeria wadda ta cewa, Manajan Daraktan Hukumar Hon. Injiniya Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana aniyar hukumar na yin hadin gwiwar yayin da yake karbar bakuncin sakatariyar zartawar hukumar ta (KACHMA) Dr Rahila Muktar a shalkwatar hukumar karota.

Hon. Faisal Mahmud ya bayyana cewa lafiyar ma’aikatan KAROTA na daga cikin abubuwan da yake baiwa muhimmanci sosai, ganin irin hadurran da ke tattare da ayyukan da suke gudanarwa.

Shugaban KAROTA ya bayyana cewa hukumar na da shirin gyara da fadada asibitin ma’aikatan da ke cikin hukumar domin ya kai ga ingantaccen mataki na aiki.

Ya yaba wa Sakatariyar Zartarwa ta KACHMA bisa wannan ziyara, inda ya tabbatar da cewa za a samu kyakkyawar hulɗa wacce za ta haifar da sakamako mai amfani.

Tun da farko, Dr Rahila Muktar ta bayyana cewa ziyararta KAROTA na da nufin kawo gudunmawar kiwon lafiya daga KACHMA har gida ga ma’aikatan hukumar.

haka kuma ta nuna jin daɗinta bisa kokarin da shugabannin KAROTA suka yi wajen samar da kayayyakin kiwon lafiya a asibitin ma’aikatan su.

Dr Rahila ta tabbatar da cewa KACHMA za ta ba da goyon baya wajen tallafa wa asibitin KAROTA domin ya kai wani mataki na ci gaba da inganci.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp