Home Labarai PDP za ta ƙaddamar da kwamitocin zartaswa na shiyoyi

PDP za ta ƙaddamar da kwamitocin zartaswa na shiyoyi

Babbar jam’iyyar adawa a Najeriya PDP na shirin kaddamar da kwamitocin zartaswa na shiyoyi da kuma kwamitin tsara zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyar na shekarar 2027 a ranar Alhamis a Abuja.

Wannan na zuwa ne yayin da ake samun rabuwar kawuna tsakanin mambobin kwamitin zartaswa na ƙasa na jam’iyar wato NEC kan yunƙurin dawo da tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan da kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, cikin jam’iyyar.

Wasu daga cikin shugabannin PDP na ganin cewa Jonathan ya bar jam’iyyar a lokaci mai muhimmanci, yayin da Obi kuma ya yi sauya sheƙa zuwa Labour, lamarin da ya rage wa jam’iyyar damar samun nasara a zaɓen 2023.

Sai dai wasu mambobin kwamitin zartaswar sun yi maraba da wannan yunƙuri, suna cewa PDP na da isassun jiga-jigai masu kwarewa waɗanda za su iya wakiltar jam’iyyar a zaɓen 2027.

Rahotanni sun tabbatar da cewa jam’iyyar ba ta kai ga tuntuɓar Jonathan da Obi a hukumance ba, sai dai wasu mutane ne daban-daban ke yin hakan a madadinta.

Kakakin jam’iyyar PDP na ƙasa, Debo Ologunagba, ya ce ƙaddamar da kwamitin zartarwar zai gudana ne a ranar Alhamis, tare da jaddada cewa jam’iyyar na da wadatattun masu neman takarar shugabanci a cikinta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp