Home Labarai PDP za ta ƙaddamar da kwamitocin zartaswa na shiyoyi

PDP za ta ƙaddamar da kwamitocin zartaswa na shiyoyi

Babbar jam’iyyar adawa a Najeriya PDP na shirin kaddamar da kwamitocin zartaswa na shiyoyi da kuma kwamitin tsara zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyar na shekarar 2027 a ranar Alhamis a Abuja.

Wannan na zuwa ne yayin da ake samun rabuwar kawuna tsakanin mambobin kwamitin zartaswa na ƙasa na jam’iyar wato NEC kan yunƙurin dawo da tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan da kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, cikin jam’iyyar.

Wasu daga cikin shugabannin PDP na ganin cewa Jonathan ya bar jam’iyyar a lokaci mai muhimmanci, yayin da Obi kuma ya yi sauya sheƙa zuwa Labour, lamarin da ya rage wa jam’iyyar damar samun nasara a zaɓen 2023.

Sai dai wasu mambobin kwamitin zartaswar sun yi maraba da wannan yunƙuri, suna cewa PDP na da isassun jiga-jigai masu kwarewa waɗanda za su iya wakiltar jam’iyyar a zaɓen 2027.

Rahotanni sun tabbatar da cewa jam’iyyar ba ta kai ga tuntuɓar Jonathan da Obi a hukumance ba, sai dai wasu mutane ne daban-daban ke yin hakan a madadinta.

Kakakin jam’iyyar PDP na ƙasa, Debo Ologunagba, ya ce ƙaddamar da kwamitin zartarwar zai gudana ne a ranar Alhamis, tare da jaddada cewa jam’iyyar na da wadatattun masu neman takarar shugabanci a cikinta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp