Home Labarai Gwamnatin Nijeriya ta rufe wurin hakar zinare a Abuja

Gwamnatin Nijeriya ta rufe wurin hakar zinare a Abuja

Gwamnatin tarayya ta bayar da umarnin rufe wurin hakar maádanai ba bisa kaída ba a Gwagwalada dake birnin tarayya Abuja, domin dakile hadarin aukuwar matsalar sauyin yanayi

Ministan ma’adanai na tarayyar Nijeriya, Dele Alake, ne ya bayar da umarni rufe wurin biyo bayan samun rahotanni na sake farfadowar ayyukan hakar zinare ba bisa ka’ída ba a yankin.

ta cikin wata sanarwa da Jaridar Economic Confidencial ta samu, wadda tace jami’an hukumar sun gudanar da wani sumame ranar 16 ga watan Agusta a yankin unguwar District 2 Extension, in da suka sami nasarar kama mutum 16 da ake zargi.

Ta cikin sanarwar mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai ga minstan Segun Tomori ya ce wannan ya biyo bayan wata zinariya da aka samu a unguwar yayin da ake hakar masai a kusa da wani gida a yankin.

ya ce dakarun lura da hakar ma’adanai, karkashin Jagorancin John Atta Onoja, sun kafa shingen bincike na tsahon sa’o’i 24 a wuraren da abin ya shafa, har sai na kammala bincike a wuri.

takardar ta ambaci Alake na jan hankalin mazauna yankin game da hadarin gurbatar muhalli ga lafiyar jama’a da ke tattare da irin wadannan ayyuka, yana mai shawartarsu da su guji shiga wuraren da abin ya shafa har sai an kammala aikin tsaftace muhalli da tabbatar da doka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp