Home Labarai An fara bincike kan hatsarin jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna

An fara bincike kan hatsarin jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna

Hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC) ta bayyana cewa an fara bincike kan hatsarin da jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna ya yi a garin Asham dake jihar Kaduna.

Hukumar ta ce binciken zai gudana ne ƙarƙashin kulawar hukumomin da abin ya shafa tare da sa ido daga ma’aikatar sufuri ta Tarayya domin gano musabbabin lamarin.

A cikin sanarwar da NRC ta fitar a ranar Talata da yamma, ta bayyana cewa jimillar mutum 618 ne suke cikin jirgin a lokacin da ya sauka daga kan layi.

Hukumar ta ce daga cikin fasinjojin, mutum bakwai ne suka samu raunuka daban-daban kuma an garzaya da su asibiti. Sauran fasinjojin kuwa an mayar da su zuwa tashoshin Idu da Kubwa ta wani jirgi da aka tura daga Abuja.

An kuma dakatar da dukkan ayyuka da zirga-zirgar jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna na ɗan lokaci, har sai an kammala aikin ceto da bincike da kuma gyara wurin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp