Home Labarai An fara bincike kan hatsarin jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna

An fara bincike kan hatsarin jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna

Hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC) ta bayyana cewa an fara bincike kan hatsarin da jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna ya yi a garin Asham dake jihar Kaduna.

Hukumar ta ce binciken zai gudana ne ƙarƙashin kulawar hukumomin da abin ya shafa tare da sa ido daga ma’aikatar sufuri ta Tarayya domin gano musabbabin lamarin.

A cikin sanarwar da NRC ta fitar a ranar Talata da yamma, ta bayyana cewa jimillar mutum 618 ne suke cikin jirgin a lokacin da ya sauka daga kan layi.

Hukumar ta ce daga cikin fasinjojin, mutum bakwai ne suka samu raunuka daban-daban kuma an garzaya da su asibiti. Sauran fasinjojin kuwa an mayar da su zuwa tashoshin Idu da Kubwa ta wani jirgi da aka tura daga Abuja.

An kuma dakatar da dukkan ayyuka da zirga-zirgar jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna na ɗan lokaci, har sai an kammala aikin ceto da bincike da kuma gyara wurin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp