Home Labarai An fara bincike kan hatsarin jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna

An fara bincike kan hatsarin jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna

Hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC) ta bayyana cewa an fara bincike kan hatsarin da jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna ya yi a garin Asham dake jihar Kaduna.

Hukumar ta ce binciken zai gudana ne ƙarƙashin kulawar hukumomin da abin ya shafa tare da sa ido daga ma’aikatar sufuri ta Tarayya domin gano musabbabin lamarin.

A cikin sanarwar da NRC ta fitar a ranar Talata da yamma, ta bayyana cewa jimillar mutum 618 ne suke cikin jirgin a lokacin da ya sauka daga kan layi.

Hukumar ta ce daga cikin fasinjojin, mutum bakwai ne suka samu raunuka daban-daban kuma an garzaya da su asibiti. Sauran fasinjojin kuwa an mayar da su zuwa tashoshin Idu da Kubwa ta wani jirgi da aka tura daga Abuja.

An kuma dakatar da dukkan ayyuka da zirga-zirgar jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna na ɗan lokaci, har sai an kammala aikin ceto da bincike da kuma gyara wurin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp