Home General NDLEA ta kama wani matashi da yayi safarar kwayoyin Tramadol dubu 7...

NDLEA ta kama wani matashi da yayi safarar kwayoyin Tramadol dubu 7 daga Legas zuwa Kano

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa reshen jihar kano ta tabbatar da kama wani matashi da take zargi da safarar kwayar Tramadol dubu 7 daga jihar legas zuwa kano.

Wannan na cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar ASN Sadiq Muhammad Maigatari ya aikewa PRNigeria a safiyar litinin 25 ga watan Agustan 2025, a madadin kwamandan rundunar ta jihar Kano.

Sanarwar ta ce Jami’an hukumar dake kiru sun sami nasarar kama wani matashi mai suna Adamu Yusuf dan shekara 29 a ranar 23 ga watan agusta a Kwanar Dangora akan hanyar sa ta shigowa Kano daga Legas dauke da kwayoyin.

Wanda ake zargin ya zuba kwayoyin da nauyin su ya kai kilogram 4.1, ne cikin wata jarkar Mai mai daukar lita 25, wannan ya nuna kokarin da hukumar ta ke na yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a Nijeriya.

daga bisani sanarwar ta yabawa jamián hukumar bisa kokarin da suka nuna, tare da yin kira da Alúmma wajen basu dukkan gudunmawar da ta kamata domin gudanar da ayyukansu na yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a jihar Kano da Nijeriya baki daya

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp