Home Labarai Gwamnatin Nijeriya ta rufe wurin hakar zinare a Abuja

Gwamnatin Nijeriya ta rufe wurin hakar zinare a Abuja

Gwamnatin tarayya ta bayar da umarnin rufe wurin hakar maádanai ba bisa kaída ba a Gwagwalada dake birnin tarayya Abuja, domin dakile hadarin aukuwar matsalar sauyin yanayi

Ministan ma’adanai na tarayyar Nijeriya, Dele Alake, ne ya bayar da umarni rufe wurin biyo bayan samun rahotanni na sake farfadowar ayyukan hakar zinare ba bisa ka’ída ba a yankin.

ta cikin wata sanarwa da Jaridar Economic Confidencial ta samu, wadda tace jami’an hukumar sun gudanar da wani sumame ranar 16 ga watan Agusta a yankin unguwar District 2 Extension, in da suka sami nasarar kama mutum 16 da ake zargi.

Ta cikin sanarwar mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai ga minstan Segun Tomori ya ce wannan ya biyo bayan wata zinariya da aka samu a unguwar yayin da ake hakar masai a kusa da wani gida a yankin.

ya ce dakarun lura da hakar ma’adanai, karkashin Jagorancin John Atta Onoja, sun kafa shingen bincike na tsahon sa’o’i 24 a wuraren da abin ya shafa, har sai na kammala bincike a wuri.

takardar ta ambaci Alake na jan hankalin mazauna yankin game da hadarin gurbatar muhalli ga lafiyar jama’a da ke tattare da irin wadannan ayyuka, yana mai shawartarsu da su guji shiga wuraren da abin ya shafa har sai an kammala aikin tsaftace muhalli da tabbatar da doka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp