Home Labarai Gwamnatin Nijeriya ta rufe wurin hakar zinare a Abuja

Gwamnatin Nijeriya ta rufe wurin hakar zinare a Abuja

Gwamnatin tarayya ta bayar da umarnin rufe wurin hakar maádanai ba bisa kaída ba a Gwagwalada dake birnin tarayya Abuja, domin dakile hadarin aukuwar matsalar sauyin yanayi

Ministan ma’adanai na tarayyar Nijeriya, Dele Alake, ne ya bayar da umarni rufe wurin biyo bayan samun rahotanni na sake farfadowar ayyukan hakar zinare ba bisa ka’ída ba a yankin.

ta cikin wata sanarwa da Jaridar Economic Confidencial ta samu, wadda tace jami’an hukumar sun gudanar da wani sumame ranar 16 ga watan Agusta a yankin unguwar District 2 Extension, in da suka sami nasarar kama mutum 16 da ake zargi.

Ta cikin sanarwar mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai ga minstan Segun Tomori ya ce wannan ya biyo bayan wata zinariya da aka samu a unguwar yayin da ake hakar masai a kusa da wani gida a yankin.

ya ce dakarun lura da hakar ma’adanai, karkashin Jagorancin John Atta Onoja, sun kafa shingen bincike na tsahon sa’o’i 24 a wuraren da abin ya shafa, har sai na kammala bincike a wuri.

takardar ta ambaci Alake na jan hankalin mazauna yankin game da hadarin gurbatar muhalli ga lafiyar jama’a da ke tattare da irin wadannan ayyuka, yana mai shawartarsu da su guji shiga wuraren da abin ya shafa har sai an kammala aikin tsaftace muhalli da tabbatar da doka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp