Home Labarai Gwamnatin tarayya ta dauki matakan dakile sake yajin aikin ASUU a Nijeriya

Gwamnatin tarayya ta dauki matakan dakile sake yajin aikin ASUU a Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Jaddada Aniyarta na Kawo Karshen Matsalolin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU)

Ministan  ilimi Dakta Tuni Al’ada ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai a birnin Abuja, inda ya ce shugaban ƙasa Bila Tinubu yana gudanar da wasu sauye-sauye, domin samun mafita ga kalubalen da ake fuskanta tsakanin kungiyar da Gwamnatin tarayya

Dakta Alausa ya ce, gwamnati ta shiga tattaunawa kai tsaye da ASUU, inda kwamitin da Yayale Ahmed ke jagoranta ya mika shawarwari, kuma an gudanar da taron manyan jami’an gwamnati domin nazari a kai.

Ministan ya bayyana cewa an kafa kwamitin kwararru bakwai karkashin Jagorancin Sakatare Janar na Ma’aikatar Ilimi, domin daidaita matsayar gwamnati kan shawarwarin da aka gabatar.

Ya jaddada cewa gwamnatin Tinubu ba za ta rattaba hannu kan yarjejeniyar da ba za ta iya aiwatarwa ba, ko ta daure Najeriya da igiyar zato.

Ministan ya kuma ce gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da ganin cewa ba a sake samun taƙaddama da ASUU ba, tare da tabbatar da cewa daliban Najeriya suna ci gaba da karatu ba tare da barazanar Yajin Aiki ba.

Ba dai wannan ne karon farko da kungiyar ASUUta yi yunkurin tsunduma yakin aiki a Nijeriyar ba sakamakon abin da take kira rashin cika mata alƙawarin da Gwamnatin tarayya ta zaga cikawa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp