Home Labarai Gwamnatin tarayya ta dauki matakan dakile sake yajin aikin ASUU a Nijeriya

Gwamnatin tarayya ta dauki matakan dakile sake yajin aikin ASUU a Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Jaddada Aniyarta na Kawo Karshen Matsalolin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU)

Ministan  ilimi Dakta Tuni Al’ada ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai a birnin Abuja, inda ya ce shugaban ƙasa Bila Tinubu yana gudanar da wasu sauye-sauye, domin samun mafita ga kalubalen da ake fuskanta tsakanin kungiyar da Gwamnatin tarayya

Dakta Alausa ya ce, gwamnati ta shiga tattaunawa kai tsaye da ASUU, inda kwamitin da Yayale Ahmed ke jagoranta ya mika shawarwari, kuma an gudanar da taron manyan jami’an gwamnati domin nazari a kai.

Ministan ya bayyana cewa an kafa kwamitin kwararru bakwai karkashin Jagorancin Sakatare Janar na Ma’aikatar Ilimi, domin daidaita matsayar gwamnati kan shawarwarin da aka gabatar.

Ya jaddada cewa gwamnatin Tinubu ba za ta rattaba hannu kan yarjejeniyar da ba za ta iya aiwatarwa ba, ko ta daure Najeriya da igiyar zato.

Ministan ya kuma ce gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da ganin cewa ba a sake samun taƙaddama da ASUU ba, tare da tabbatar da cewa daliban Najeriya suna ci gaba da karatu ba tare da barazanar Yajin Aiki ba.

Ba dai wannan ne karon farko da kungiyar ASUUta yi yunkurin tsunduma yakin aiki a Nijeriyar ba sakamakon abin da take kira rashin cika mata alƙawarin da Gwamnatin tarayya ta zaga cikawa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp