Home General Hukumar DSS ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru

Hukumar DSS ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru

Hukumar DSS a Najeriya ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru da ta kama a watan da ya gabata, yayin da ake tuhumarsu da laifukan ta’addanci a babbar kotun tarayya da ke Abuja.

Waɗanda ake zargin sun haɗar da Mahmud Usman wanda aka fi sani da Abu Bara’a sai kuma Mahmud Al-Nigeri, wanda aka fi sani da Malam Mamuda.

Tuni hukumar ta shigar da ƙararraki guda 32 kan mutanen gaban mai shari’a Emeka Nwite.

Tuhumar da ake yiwa mutanen biyu akwai zargin haɗa kai da kuma tsarawa tare da ƙaddamar da hari kan gidan yarin kuje a watan Yulin 2022, wanda ya baiwa ɗaurarru sama da 600 damar tserewa.

Haka kuma sune ake zargi da kai hari kan barikin sojoji na Wawa da ke Kainji da ke jihar Naija, inda aka tafka asarar rayuka da dukiyoyi.

Hukumar ta DSS ta ce rahoton binciken ya nuna yadda waɗannan mayaƙa suka karɓi horo na musamman a sansanonin ƴan ta’adda da ke ƙasashen Mali da kuma Libya kan ƙaddamar da hari, sarrafa makamai da kuma dubarun yaƙi.

Mahmuda kuwa ya karɓi wani horo mai matuƙar haɗari a tsakanin shekarar 2013 zuwa 2015 a hannun wata ƙungiyar ta’addanci ta ƙasa da ƙasa.

DSS ta kuma ce waɗannan mutane biyu sune suka jagoranci manyan hare-haren ta’addanci da garkuwa da mutane ciki har da ɗaya daga cikin injiniyoyin ƙasar Faransa da ke aiki a Najeriya Francis Collomp a shekarar 2013 da kuma Alhaji Musa Umar Uba Magajin Daura a 2019.

Waɗannan mutane ne kuma suka kai hari kan guda daga cikin kamfanonin sarrafa Uranium a jamhuriyar Nijar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp