Home Labarai Rundunar ƴan sandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami’anta a Jihar Benue

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami’anta a Jihar Benue

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta tabbatar da kashe jami’anta uku tare da bacewar wasu bakwai a wani mummunan harin kwantan bauna da aka kai wa rundunar kota-kwananta a jihar Benue.

A ranar Laraba 10 ga watan Satumban 2025 ne, aka kai wani hari makamancinsa a garin Egbe da ke ƙaramar hukumar Yagba ta yamma da ke jihar Kogi, a kusa da kan iyakar ta da jihar Kwara, inda jami’anta uku suka mutu.

Yayin da Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kogi, William Aya, ya tabbatar da mutuwar jami’an rundunar guda uku, sannan kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Miller Dantawaye, ya ce an tura tawagar da za ta mayar da martani zuwa yankin.

A wata sanarwa da rundunar ta fitar mai ɗauke da sa hannun jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, CSP Benjamin Hundeyin, a ranar Lahadi, ta ce ‘yan sandan sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar Juma’a, 19 ga watan Satumbar, 2025, a ƙaramar hukumar Katsina-Ala, inda inda ake kyautata zaton ‘yan bindigar yankin ne suka ƙaddamar da harin.

Kakakin ‘yan sandan ya ce an kama mutane shida da ake zargi a wani samame da ake ci gaba da kai wa kuma suna taimakawa da bayanai masu amfani.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp