Home Labarai Rundunar ƴan sandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami’anta a Jihar Benue

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami’anta a Jihar Benue

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta tabbatar da kashe jami’anta uku tare da bacewar wasu bakwai a wani mummunan harin kwantan bauna da aka kai wa rundunar kota-kwananta a jihar Benue.

A ranar Laraba 10 ga watan Satumban 2025 ne, aka kai wani hari makamancinsa a garin Egbe da ke ƙaramar hukumar Yagba ta yamma da ke jihar Kogi, a kusa da kan iyakar ta da jihar Kwara, inda jami’anta uku suka mutu.

Yayin da Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kogi, William Aya, ya tabbatar da mutuwar jami’an rundunar guda uku, sannan kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Miller Dantawaye, ya ce an tura tawagar da za ta mayar da martani zuwa yankin.

A wata sanarwa da rundunar ta fitar mai ɗauke da sa hannun jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, CSP Benjamin Hundeyin, a ranar Lahadi, ta ce ‘yan sandan sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar Juma’a, 19 ga watan Satumbar, 2025, a ƙaramar hukumar Katsina-Ala, inda inda ake kyautata zaton ‘yan bindigar yankin ne suka ƙaddamar da harin.

Kakakin ‘yan sandan ya ce an kama mutane shida da ake zargi a wani samame da ake ci gaba da kai wa kuma suna taimakawa da bayanai masu amfani.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp