Home Labarai Ƴan bindiga sun sako mutane 40 bayan sulhu da mahukuntan Katsina

Ƴan bindiga sun sako mutane 40 bayan sulhu da mahukuntan Katsina

Taswirar Katsina

Aƙalla mutane 40 da aka yi garkuwa da su ne suka shaƙi iskar ƴanci a ƙaramar hukumar Faskari ta jihar Katsina bayan tattaunawa tsakanin ƙasurgumin ɗan bindigar daji Isya Kwashen Garwa da mahukuntan jihar inda yaran ɗan ta’addar suka miƙa mutanen ga hukumomin jihar.

Bayanai sun ce sakin wannan adadi na zuwa ne bayan sakin wasu mutane 30 a Larabar makon jiya da kuma wasu mutum biyu na daban, wanda ke nuna a jumlace ɗan bindigar ya sako mutane 72 daga faro wannan tattaunawa kawo yanzu.

Mahukuntan Katsina na sahun waɗanda ke tattaunawa da ƴan bindiga don kawo ƙarshen tashe-tashen hankulan da jihar ke gani, sai dai a gefe guda ana ci gaba da ganin ta’adin waɗannan ɓatagari.

Mataimakin shugaban karamar hukumar Faskari, Hon. Isiyaku Wada ya tabbatar da sakin mutanen, to sai dai ya buƙaci haɗin-kan jami’an tsaro don tabbatar da samun nasarar wannan sulhu da ke bai wa kowane bangare damar yin walwala.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp