Home Labarai Gwamnan Enugu ya koma APC bayan ficewa daga PDP

Gwamnan Enugu ya koma APC bayan ficewa daga PDP

Gwamnan jihar Enugu, Peter Mbah ya fice daga jam’iyyarsa ta PDP tare da komawa APC mai mulkin Najeriya.

Mista Mbah ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai da ya shirya a fadar gwamnanatin jihar da ke birnin Enugu.

“Bayan dogon lokaci da muka ɗauka muna nazari, a yau mun yanke shawarar ficewa daga PDP tare da komawa APC,” kamar yadda gwamnan ya bayyana.

Mbah ya ce ya koma APC ne saboda kyawawan manufofin jam’iyyar da ayyukan ci gaba da take samarwa a Najeriya da ma jiharsa ta Enugu.

Gwamnan ya ce yana da ƙwarin gwiwar cewa komawarsa APC za ta samar wa jihar ƙarin damarmaki da ci gaba.

Taron ya samu halartar manyan ƴansiyasar jihar da suka haɗa da mataimakin gwamnan jihar, Barr Ifeanyi Ossai da tsoffin gwamnonin jihar, Sullivan Chime da Rt Hon. ifeanyi Ugwuanyi,da Tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Chief Ken Nnamani, da tsoffin ƴanmajalisar tarayya daga jihar da kuma masu ci, da shugaban majalisar dokokin jihar da shugaban jam’iyyar APC na jihar, da sauran muƙarraban gwamnatinsa, kamar yadda mataimaki na musamman ga gwamnan kan kafofin yaɗa labarai, Dan Nwomeh ya wallafa a shafinsa na X.

Dama dai tun jiya wasu daga cikin kwamishinonin gwamnan suka fice daga PDP tare da komawa APC.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp