Home General Gwamnatin Najeriya ta cire darasin Lissafi cikin sharuɗan samun gurbin karatun Jami’a...

Gwamnatin Najeriya ta cire darasin Lissafi cikin sharuɗan samun gurbin karatun Jami’a ga wasu ɗaliban

Gwamnatin Najeriya ta cire wajibcin cin darasin lissafi cikin sharuɗaɗan samun gurbin karatu a jami’a ga ɗaliban da za su karanci kwasa-kwasan da na na kimiyya ba.

Cikin wata sanarwar da ma’aikatar ilimin ƙasar ta fitar ta ce daga yanzu ɗaliban da ke son karanta kwasa-kwasan da ba su da kusanci da kimiyya ko fasaha ba, cin darasin lissafi a sakandire bai zame musu wajibi ba.

Kwasa-kwasan sun haɗa da nazarin ilimin harsuna da zane-zane da nazarin wasannin kwaikwayo da kaɗe-kaɗe, amma dole sai sun ci darasin Ingilishi a sakandire.

Sai dai sanarwar ta jaddada wajibcin darasin lissafin ga sauran kwasa-kwasan da suka shafi kimiyya da fasaha da nazarin zamantakewa.

Ma’aikatar ta ce ta ɗauki matakin ne domin ɗalibai da dama su riƙa samun damar shiga jami’a.

”Matakin zai samar da ƙarin guraben karatu 300,000 a kowace shekara, domin rage yawan ɗaliban da ba sa samun guraben karatu, tare da ƙarfafa sana’o’in dogaro da kai”, in ji sanarwar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp