Home Labarai Babu wasu bayanan an yi wa masu bin wani addini kisan ƙare...

Babu wasu bayanan an yi wa masu bin wani addini kisan ƙare dangi – Sultan

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya bayyana cewa babu wasu bayanan da ke nuna cewa an yi wa masu bin wani addini ko Kirista ko Musulmi kisan ƙare dangi a Najeriya.

Sarkin ya faɗi hakan ne a yayin buɗe taron Majalisar Sarakunan Arewa a Birnin Kebbi, 2025.

Sarkin ya ce, “Babu yadda za a kashe wani mutum, ko Musulmi ko Kirista, ba tare da sanin sarakuna ko shugabannin al’ummar da wannan mutumin ya fito ba.”

Ya kuma ƙalubalanci kowa, a cikin gida ko waje, da su kawo hujja ta gaske kan wani kisan ƙare dangi a Najeriya.”

Sultan Sa’ad ya gargadi jama’a da kada su gaskata duk abin da suka gani ko karanta a kafafen sada zumunta, yana mai cewa yawancin bayanan da ake yaɗawa ba gaskiya bane.

“Yawancin abin da aka wallafa a kafafen sada zumunta ba gaskiya bane. Dole mutane su tabbatar da sahihancin bayani kafin su ɗauke shi a matsayin gaskiya,” in ji shi.

Sarkin ya bukaci Gwamnatin Tarayya da ta hanzarta tsara dokoki da za su kula da ayyukan masu amfani da kafafen sada zumunta domin rage yaɗa labaran ƙarya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp