Gwamnan Jihar Katsina ya samar sabuwar ma’aikata a jihar

Gwamna Jihar Katsina Dikko Radda ya amince da yin garambawul a kunshin majalisar zartarwar jihar tare da ƙirƙirar sabuwar ma’aikata da zata lura da harkokin kiwo a jihar.

Mai magana da yawun gwamnan, Malam Ibrahim Kaula-Mohammed, ne ya bayyana hakan ga manema labarai ranar Asabar a Katsina.

Ya ce Alhaji Adnan Nahabu an sauya masa Ma’aikata daga ta Harkokin Musamman zuwa Ma’aikatar Ilimin Gaba da Sakandare, Sana’o’i da Fasaha a matsayin Kwamishina.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com