Home Labarai Dalilin Tinubu na soke afuwar da Ya yiwa Maryam Sanda

Dalilin Tinubu na soke afuwar da Ya yiwa Maryam Sanda

 Jaridar The Punch ta ruwaito cewa bayan yawan suka da cece-kuce daga jama’a kan sahihancin afuwar, shugaban ƙasa ya soke cikakkiyar afuwar, tare da mayar da hukuncin zuwa daurin shekaru 12 a gidan yari.

A watan Afrilu 2020 ne kotu ta samu Maryam Sanda da laifin kashe mijinta, ɗan siyasa kuma ɗan gidan tsohon shugaban jam’iyyar PDP, Haliru Bello, bayan muhawara ta cikin gida ta kai ga rikici.

A lokacin bikin ranar ‘yancin kai ta bana, an saka sunanta cikin jerin mutanen da shugaban ƙasa ya ba wa afuwa, lamarin da ya jawo matsanancin bacin rai daga jama’a, musamman daga kungiyoyin kare haƙƙin mata da iyalai.

Wata majiya daga fadar shugaban ƙasa ta tabbatar wa da manema labarai cewa an duba batun afuwar nan daga farko, kuma aka yanke shawarar a soke ta domin tabbatar da adalcinta ga waɗanda abin ya shafa.

Da wannan sabon mataki, Maryam Sanda za ta ci gaba da zaman gidan yari na shekaru 12, bisa umarnin da fadar shugaban ƙasa ta tabbatar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp