Home Labarai Dalilin Tinubu na soke afuwar da Ya yiwa Maryam Sanda

Dalilin Tinubu na soke afuwar da Ya yiwa Maryam Sanda

 Jaridar The Punch ta ruwaito cewa bayan yawan suka da cece-kuce daga jama’a kan sahihancin afuwar, shugaban ƙasa ya soke cikakkiyar afuwar, tare da mayar da hukuncin zuwa daurin shekaru 12 a gidan yari.

A watan Afrilu 2020 ne kotu ta samu Maryam Sanda da laifin kashe mijinta, ɗan siyasa kuma ɗan gidan tsohon shugaban jam’iyyar PDP, Haliru Bello, bayan muhawara ta cikin gida ta kai ga rikici.

A lokacin bikin ranar ‘yancin kai ta bana, an saka sunanta cikin jerin mutanen da shugaban ƙasa ya ba wa afuwa, lamarin da ya jawo matsanancin bacin rai daga jama’a, musamman daga kungiyoyin kare haƙƙin mata da iyalai.

Wata majiya daga fadar shugaban ƙasa ta tabbatar wa da manema labarai cewa an duba batun afuwar nan daga farko, kuma aka yanke shawarar a soke ta domin tabbatar da adalcinta ga waɗanda abin ya shafa.

Da wannan sabon mataki, Maryam Sanda za ta ci gaba da zaman gidan yari na shekaru 12, bisa umarnin da fadar shugaban ƙasa ta tabbatar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp