Home Labarai Ma’aikatan lantarki sun yi barazanar katse wuta a faɗin Najeriya

Ma’aikatan lantarki sun yi barazanar katse wuta a faɗin Najeriya

Ƙungiyar ma’aikatan lantarki ta Najeriya (NUEE) ta yi barazanar katse wuta a faɗin ƙasar, sakamakon zargin da take yi na cewa an kai wa ma’aikatan kamfanin rarraba lantarki na ƙasar hari.

Cikin wata sanarwa da muƙaddashin babban sakataren ƙungiyar, Dominic Igwebike ya fitar, ya ce hakan ya zama wajibi ne bayan zargin wasu ƴansanda da ke aiki bisa umurnin gwamnatin jiha, sun yi wa ma’aikatan da ke aiki a cibiyar lantarki ta Egbu da ke Jihar Imo duka, da yi musu barazana da bindiga da kuma garkuwa da wasu.

A cewar sa ƴan sandan sun shiga cibiyar ne da ƙarfin tsiya, tare da lalata kayayyakin aiki da dakatar da ayyukan da ake gudanarwa, kamar yadda kafar talibijin ta channels ta ruwaito.

A cewar sanarwar, ƙungiyar ta riga ta bai wa mambobinta umurnin katse samar da lantarki a jihar Imo har sai wani lokaci.

Ta kuma yi barazanar katse aiki a faɗin Najeriya har sai hukumomi sun ɗauki matakan gaggawa na tabbatar da tsaron ma’aikatan lantarki a faɗin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp