Home Labarai SERAP ta buƙaci CBN ya dawo da Naira triliyan 3 da ake...

SERAP ta buƙaci CBN ya dawo da Naira triliyan 3 da ake zargin sun yi ɓatan dabo

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Jama’a da Kula da Al’amuran Tattalin Arziki (SERAP), ta bai wa Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Olayemi Cardoso, kwanaki bakwai da ya fitar da bayanai kan Naira Tiriliyan 3 na kuɗaɗen al’umma da ake zargin sun yi batan dabo.

Ƙungiyar ta bayyana cewa wannan lamari na zuwa ne bayan wani rahoton Babban Ma’ajin Kasa na shekara ta 2022, wanda ya buƙaci CBN ya bayyana inda kuɗaɗen suka shiga.

Rahoton ya nuna akwai matsalar ɓacewar rarar kudi da basukan da ba a biya ba da kuma kwangiloli masu cike da ayoyin tambaya.

SERAP ta ce CBN ya gaza tura sama da naira triliyan 1 da biliyan 440 na rarar kudi na gwamnatin tarayya zuwa asusun kuɗaɗen shiga na bai ɗaya.

A sanarwar da ta fitar, SERAP ta lura cewa CBN bai karɓo sama da naira biliyan 700 ba na basussukan da kuɗaden kai dauki da aka bayar tsakanin 2018 zuwa Mayun 2022 ba.

Haka kuma CBN ya bayar da kwangiloli 43, na sama da Naira biliyan 189, sai dai ƴan kwangilar sun yi jinkiri da gangan inda daga baya suka buƙaci a sauya farashin kwangilar wanda ya kai ga biyan kuɗi fiye da Naira biliyan 9 ba bisa ƙa’ida ba.

Tana kuma fargabar za a iya karkatar da waɗannan kudaɗen don haka ne ta nemi a gaggauta dawo da su baitul malin gwamnati, ko ta ɗauki matakin shari’ah.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp