Home Labarai SERAP ta buƙaci CBN ya dawo da Naira triliyan 3 da ake...

SERAP ta buƙaci CBN ya dawo da Naira triliyan 3 da ake zargin sun yi ɓatan dabo

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Jama’a da Kula da Al’amuran Tattalin Arziki (SERAP), ta bai wa Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Olayemi Cardoso, kwanaki bakwai da ya fitar da bayanai kan Naira Tiriliyan 3 na kuɗaɗen al’umma da ake zargin sun yi batan dabo.

Ƙungiyar ta bayyana cewa wannan lamari na zuwa ne bayan wani rahoton Babban Ma’ajin Kasa na shekara ta 2022, wanda ya buƙaci CBN ya bayyana inda kuɗaɗen suka shiga.

Rahoton ya nuna akwai matsalar ɓacewar rarar kudi da basukan da ba a biya ba da kuma kwangiloli masu cike da ayoyin tambaya.

SERAP ta ce CBN ya gaza tura sama da naira triliyan 1 da biliyan 440 na rarar kudi na gwamnatin tarayya zuwa asusun kuɗaɗen shiga na bai ɗaya.

A sanarwar da ta fitar, SERAP ta lura cewa CBN bai karɓo sama da naira biliyan 700 ba na basussukan da kuɗaden kai dauki da aka bayar tsakanin 2018 zuwa Mayun 2022 ba.

Haka kuma CBN ya bayar da kwangiloli 43, na sama da Naira biliyan 189, sai dai ƴan kwangilar sun yi jinkiri da gangan inda daga baya suka buƙaci a sauya farashin kwangilar wanda ya kai ga biyan kuɗi fiye da Naira biliyan 9 ba bisa ƙa’ida ba.

Tana kuma fargabar za a iya karkatar da waɗannan kudaɗen don haka ne ta nemi a gaggauta dawo da su baitul malin gwamnati, ko ta ɗauki matakin shari’ah.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp