Home Labarai Rundunar ‘yan sanda Abuja ta Musanta yunkurin hallaka Lt. Ahmed Yerima

Rundunar ‘yan sanda Abuja ta Musanta yunkurin hallaka Lt. Ahmed Yerima

Rundunar ƴansandan birnin Abuja, ta musanta wani iƙirari dake cewa wasu ‘yan bindiga sun yi yunkurin hallaka Laftanar Ahmed Yerima.

Wannan na cikin wata sanarwa da rundunar ƴansandan Najeriya, reshen birnin na Abuja ta fitar ta hannun kakakinta, SP Josephine Adeh,  in da ta ce babu inda aka samu irin wannan iƙirari, labara ne kawai da bashi da tushe ballantana makama.

Da yammacin ranar Lahadi ne rahotonin yunƙurin kashe Laftanar Ahmed Yerima – matashin sojan da ya yi sa-in-sa da ministan Abuja, Nyesom Wike a makon da ya gabata – suka cika shafukan sada zumunta.

Rahotonnin sun yi iƙirarin cewa wasu matasa ne da ba a san ko su wane ne ba suka yi yunƙurin halaka sojan ruwan a Abuja, babban birnin ƙasar.

”Rundunar ƴansanda reshen Abuja ta lura da abubuwan da ke yawo a shafukan sada zumunta, da ke zargin an yi yunƙurin kashe Lt. Ahmed Yerima.

“Rundunar na son bayyana wa al’umma cewa ba mu samu wasu bayanai game da iƙirarin da ake yaɗawa ba ɗaukacin yankin Babban Birnin Tarayya,” in ji SP Josephine Adeh.

Daga bisani rundunar ‘yansandan ta shawarci al’umma su guji yaɗa labaran da ba su da tabbaci a kansu, saboda a cewarta babu abin da hakan ke haifarwa sai tayar da hankula.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp