Home Labarai Rundunar ‘yan sanda Abuja ta Musanta yunkurin hallaka Lt. Ahmed Yerima

Rundunar ‘yan sanda Abuja ta Musanta yunkurin hallaka Lt. Ahmed Yerima

Rundunar ƴansandan birnin Abuja, ta musanta wani iƙirari dake cewa wasu ‘yan bindiga sun yi yunkurin hallaka Laftanar Ahmed Yerima.

Wannan na cikin wata sanarwa da rundunar ƴansandan Najeriya, reshen birnin na Abuja ta fitar ta hannun kakakinta, SP Josephine Adeh,  in da ta ce babu inda aka samu irin wannan iƙirari, labara ne kawai da bashi da tushe ballantana makama.

Da yammacin ranar Lahadi ne rahotonin yunƙurin kashe Laftanar Ahmed Yerima – matashin sojan da ya yi sa-in-sa da ministan Abuja, Nyesom Wike a makon da ya gabata – suka cika shafukan sada zumunta.

Rahotonnin sun yi iƙirarin cewa wasu matasa ne da ba a san ko su wane ne ba suka yi yunƙurin halaka sojan ruwan a Abuja, babban birnin ƙasar.

”Rundunar ƴansanda reshen Abuja ta lura da abubuwan da ke yawo a shafukan sada zumunta, da ke zargin an yi yunƙurin kashe Lt. Ahmed Yerima.

“Rundunar na son bayyana wa al’umma cewa ba mu samu wasu bayanai game da iƙirarin da ake yaɗawa ba ɗaukacin yankin Babban Birnin Tarayya,” in ji SP Josephine Adeh.

Daga bisani rundunar ‘yansandan ta shawarci al’umma su guji yaɗa labaran da ba su da tabbaci a kansu, saboda a cewarta babu abin da hakan ke haifarwa sai tayar da hankula.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp