Har yanzu ba’a gama tantance adadin daliban da aka sace a jihar Neja ba

Bayanai daga jihar Neja na cewa maharan da suka sace ɗaliban makarantar St. Mary a kan babura suka je.

Sarkin Papiri, inda lamari ya faru ya shaida wa BBC cewa maharan sun je garin ne a kan babura inda suka karkasu.

”Wasu sun tsaya a bakin kasuwa, wasu kuma suka isa makarantar, inda suka harbe maigadin makarantar, wanda yanzu haka ke kwance a asibiti”,in ji shi.

Ya ce kawo yanzu ba a san adadin ɗaliban da aka sace be.

”Har yanzu ba a gama tantance adadin ɗaliban da aka sace ba, sai zuwa an jima ne in an kammala za a fitar da sunayen ɗaliban”, kamar yadda ya yi ƙarin haske.

Ya ƙara da cewa al’ummar garin na cikin tashin hankali da ɗimauta, tun bayan aukuwar harin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com