Home Labarai Har yanzu ba’a gama tantance adadin daliban da aka sace a jihar...

Har yanzu ba’a gama tantance adadin daliban da aka sace a jihar Neja ba

Bayanai daga jihar Neja na cewa maharan da suka sace ɗaliban makarantar St. Mary a kan babura suka je.

Sarkin Papiri, inda lamari ya faru ya shaida wa BBC cewa maharan sun je garin ne a kan babura inda suka karkasu.

”Wasu sun tsaya a bakin kasuwa, wasu kuma suka isa makarantar, inda suka harbe maigadin makarantar, wanda yanzu haka ke kwance a asibiti”,in ji shi.

Ya ce kawo yanzu ba a san adadin ɗaliban da aka sace be.

”Har yanzu ba a gama tantance adadin ɗaliban da aka sace ba, sai zuwa an jima ne in an kammala za a fitar da sunayen ɗaliban”, kamar yadda ya yi ƙarin haske.

Ya ƙara da cewa al’ummar garin na cikin tashin hankali da ɗimauta, tun bayan aukuwar harin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp