Home Labarai ACM ta yi Ala-wadai da satar dalibai a Neja

ACM ta yi Ala-wadai da satar dalibai a Neja

Kungiyar Arewa Connect Movement ta bayyana bakin ciki kan sabon harin da yan bindiga suka kai Makarantar Katolika ta St. Mary’s da ke kauyen Papiri a Karamar Hukumar Agwara ta Jihar Neja, inda suka yi awon gaba dalibai da ma’aikata da ba a san yawan su ba.

Kungiyar ta ce wannan lamari babban tashin hankali ne ga iyaye, yan uwa da kuma al’ummar kasa baki ɗaya.

A cikin sanarwar da shugaban kungiyar, Auwal Mahmud Durumin Iya, ya fitar, ya bayyana cewa a kwanan nan irin wannan abu ya faru inda aka sace dalibai mata 25 a Jihar Kebbi, kuma har yanzu ba a samu wani cigaba a kan lamarin ba, inda ya ce sake faruwar irin wannan al’amari a cikin lokaci kankani na sake nuna yadda matsalar tsaro ke kara ta’azzara.

Kungiyar ta bayyana cewa wannan kalubale ne babba ga gwamnati da hukumomin tsaro, tare da kira gare su da su sauya dabarun yaki da yan ta’adda domin kawo karshen wannan ta’asa wacce ta dade tana addabar al’umma.

A karshe, kungiyar ta mika sakon jaje ga Gwamnatin Tarayya, jihohin Neja da Kebbi, iyayen yara, da al’ummar ƙasa baki daya, tana mai rokon ALLAH Ya kawo dauki cikin gaggawa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp