Tinubu ya fasa zuwa taron G20 saboda sace ɗalibai a makarantu

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya fasa zuwa taron G20 na ƙasashe masu ƙarfin masana’atu a duniya, sakamakon matsalar satar ɗalibai a ƙasar .

Cikin wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar ta fitar ta ce shugaban ya ɗauki matakin ne sakamakon halin da ake ciki a ƙasar na satar ɗalibai a makarantu.

A maimakon haka Shugaba Tinubu ya tura mataimakinsa Kashim Shettima domin ya wakilce shi a taron.

Tun da farko fadar shugaban ƙasar ta ce Tinubu ya ɗage tafiyarsa zuwa taron sakamakon sanin halin da ake ciki game da satar ɗalibai a Kebbi da masu ibada a jihar Kwara.

An tsara gudanar da taron ne a yau Asabar 22 ga watan Nuwamban 2025.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com