Amurka ta fara kai harin soji Arewacin Nijeriya

Shugaba Donald Trump ya ce Amurka ta ƙaddamar da wani mummunan hari kan mayakan IS a arewa maso yammacin Najeriya.

“Dakarun Amurka sun ƙaddamar da hare-hare masu kyau,” in ji Trump.

Cibiyar sojin Amurka a Afrika daga baya ta ce an kai hare-haren ne a jihar Sokoto.

Shugaban ya zargi ƙungiyar da kai hari tare da kashe Kiristocin da ba su ji ba su gani ba a ƙasar.

A shafinsa na Social Truth, Trump ya wallafa da yammacin Alhamis cewa “a ƙaƙashin shugabancina, ƙasarmu ba za ta bar masu tsattsauran ra’ayin Musulunci sun girmama ba.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com