Home Labarai Nan gaba za ku ga Amfanin dokar haraji -Tinubu

Nan gaba za ku ga Amfanin dokar haraji -Tinubu

Shugaba Tinubu na Najeriya ya ce idan ƴan Najeriya suka yi haƙuri za a samu rayuwa mai inganci ta hanyar alkilta arziƙin ƙasa yadda ya kamata abin da zai sa ƙasar ta yi fice a duniya a wannan sabuwar shekara ta 2026.

Tinubu ya shaida hakan ne a saƙon sabuwar shekara da ya fitar ranar Alhamis inda ya ƙara da cewa gwamnatinsa ci gaba da gini a kan abin da ta fara na sauye-sauye masu alkairi ga ƴan Najeriya.

“Duk da irin ƙalubalen da duniya ke fuskanta ta fuskar tattalin arziƙi, mun samu gagarumar nasara a 2025 musamman a fannin tattalin arziƙi”.

Dangane kuma da sabuwar dokar haraji da ta fara aiki, Tinubu ya nemi ƴan Najeriya da su ƙara hakuri domin nan gaba kaɗa za su ga alkairin tsarin.

Ya kuma ce ɗaya daga cikin dailan aiwatar da wannan sabon tsarin harajin shi ne kawo sauyi wajen tatsar ƴan Najeriya harajin da ya wuce ƙima.

“Muna kuma son kawo ƙarshen biyan haraji da yawa inda dukkan matakan gwamnati kan karɓi haraji. Na yaba wa jihohin da suka amince da shiga tsarin harajin na bai ɗaya domin sauwaƙe wa jama’a yawan haraje-haraje a kan al’umma da kayan abinci.”

“Sabuwar shekarar ta fara da aiwatar da sauye-sauyen harajin da aka yi domin dasa harsashin Najeriya mai adalci da kuma ƙarfi a fannin kudaɗen shiga,” in ji Tinubu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp