Home Labarai Nan gaba za ku ga Amfanin dokar haraji -Tinubu

Nan gaba za ku ga Amfanin dokar haraji -Tinubu

Shugaba Tinubu na Najeriya ya ce idan ƴan Najeriya suka yi haƙuri za a samu rayuwa mai inganci ta hanyar alkilta arziƙin ƙasa yadda ya kamata abin da zai sa ƙasar ta yi fice a duniya a wannan sabuwar shekara ta 2026.

Tinubu ya shaida hakan ne a saƙon sabuwar shekara da ya fitar ranar Alhamis inda ya ƙara da cewa gwamnatinsa ci gaba da gini a kan abin da ta fara na sauye-sauye masu alkairi ga ƴan Najeriya.

“Duk da irin ƙalubalen da duniya ke fuskanta ta fuskar tattalin arziƙi, mun samu gagarumar nasara a 2025 musamman a fannin tattalin arziƙi”.

Dangane kuma da sabuwar dokar haraji da ta fara aiki, Tinubu ya nemi ƴan Najeriya da su ƙara hakuri domin nan gaba kaɗa za su ga alkairin tsarin.

Ya kuma ce ɗaya daga cikin dailan aiwatar da wannan sabon tsarin harajin shi ne kawo sauyi wajen tatsar ƴan Najeriya harajin da ya wuce ƙima.

“Muna kuma son kawo ƙarshen biyan haraji da yawa inda dukkan matakan gwamnati kan karɓi haraji. Na yaba wa jihohin da suka amince da shiga tsarin harajin na bai ɗaya domin sauwaƙe wa jama’a yawan haraje-haraje a kan al’umma da kayan abinci.”

“Sabuwar shekarar ta fara da aiwatar da sauye-sauyen harajin da aka yi domin dasa harsashin Najeriya mai adalci da kuma ƙarfi a fannin kudaɗen shiga,” in ji Tinubu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp