Home Labarai Sojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu da aka sace...

Sojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu da aka sace a Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta na Operation Haɗin Kai sun samu nasarar kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu fararen hula da aka sace a wani samame da suka kai a karamar hukumar Konduga, Jihar Borno.

Sojojin, tare da haɗin gwiwar dakarun ƴan sa kai ta CJTF, sun yaƙi ƴanbindigar ne a kan hanyar Sojiri a safiyar ranar 4 ga Janairu, 2026.

Rundunar ce ta bayyana hakan a shafinta na X.

A yayin samamen, an kashe ƴanbindiga guda biyar yayin da suka ceto mtum 3 da aka sace ba tare da asarar rai daga bangaren sojoji ba.

Haka kuma, sojojin sun ƙwato bindigogi na AK-47 da wasu kayan yaki daban-daban.

Rundunar ta ce wannan aiki ya nuna jajircewar sojojin Najeriya wajen kai farmaki kan ƴanbindiga, yayin da suke mai da hankali wajen kare rayukan fararen hula da tabbatar da tsaro a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp