Home Labarai Sojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu da aka sace...

Sojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu da aka sace a Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta na Operation Haɗin Kai sun samu nasarar kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu fararen hula da aka sace a wani samame da suka kai a karamar hukumar Konduga, Jihar Borno.

Sojojin, tare da haɗin gwiwar dakarun ƴan sa kai ta CJTF, sun yaƙi ƴanbindigar ne a kan hanyar Sojiri a safiyar ranar 4 ga Janairu, 2026.

Rundunar ce ta bayyana hakan a shafinta na X.

A yayin samamen, an kashe ƴanbindiga guda biyar yayin da suka ceto mtum 3 da aka sace ba tare da asarar rai daga bangaren sojoji ba.

Haka kuma, sojojin sun ƙwato bindigogi na AK-47 da wasu kayan yaki daban-daban.

Rundunar ta ce wannan aiki ya nuna jajircewar sojojin Najeriya wajen kai farmaki kan ƴanbindiga, yayin da suke mai da hankali wajen kare rayukan fararen hula da tabbatar da tsaro a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp