Home Labarai Sojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu da aka sace...

Sojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu da aka sace a Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta na Operation Haɗin Kai sun samu nasarar kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu fararen hula da aka sace a wani samame da suka kai a karamar hukumar Konduga, Jihar Borno.

Sojojin, tare da haɗin gwiwar dakarun ƴan sa kai ta CJTF, sun yaƙi ƴanbindigar ne a kan hanyar Sojiri a safiyar ranar 4 ga Janairu, 2026.

Rundunar ce ta bayyana hakan a shafinta na X.

A yayin samamen, an kashe ƴanbindiga guda biyar yayin da suka ceto mtum 3 da aka sace ba tare da asarar rai daga bangaren sojoji ba.

Haka kuma, sojojin sun ƙwato bindigogi na AK-47 da wasu kayan yaki daban-daban.

Rundunar ta ce wannan aiki ya nuna jajircewar sojojin Najeriya wajen kai farmaki kan ƴanbindiga, yayin da suke mai da hankali wajen kare rayukan fararen hula da tabbatar da tsaro a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp