Home Labarai Sojoji sun daƙile yunƙurin harin ƴanbidiga a Borno

Sojoji sun daƙile yunƙurin harin ƴanbidiga a Borno

Nigerian Army

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta na Operation Haɗin Kai daƙile yaƙunrin hain ƴanbindiga ina sun kashe su daga tsaunukan Mandara a lokacin da suka yunƙurin kai hari a cikin al’ummar Bitta da ke Borno.

Rundunar ce ta sanar da hakan a shafinta na X inda ta ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 12:30 na tsakar daren ranar 18 ga Disamba, 2025 lokacin da sojojin suka gano wannan yunƙuri na ‘yanbindig da ke tafiya zuwa yankin.

A cewar rundunar, sai da sojojin suka bari ƴanbindigar suka shiga wani yanki da aka musu tarko kafin buɗe musu wuta, inda suka kashe wasu daga cikin maharan, ciki har da wani kwamandansu da mai ɗaukar musu hoto.

Rundunar ta ƙara da cewa, daga baya rundunar sojojin sama ta Operation Haɗin Kai ta kai farmaki kan waɗanda suka tsere lamarin da ya ƙara hallaka wasu tare da tarwatsa hanyoyin gudunsu.

A lokacin da ake fafatawa a yankin, an ruwaito cewa sojoji sun bi diddigin hanyoyi da dama, kuma sun gano kaburbura marasa zurfi, wanda ke nuna ƙarin asarar rayuka da aka yi wa ‘yan ta’addan a lokacin fafatawar.

Bayan fafatawar, sojoji sun gudanar da bincike a yankin inda suka ƙwato kayayyaki da makamai da dama.

Rundunar ta ce sojoji na ci gaba da ayyukansu domin hana masu ta da ƙayar baya samun damar kai hari, tare da tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp