Home Labarai Gwamnatin Najeriya ta dakatar da fara aikin sabuwar dokar haraji

Gwamnatin Najeriya ta dakatar da fara aikin sabuwar dokar haraji

Gwamnatin Najeriya ta dakatar da tsare-tsare da za a yi amfani da su wajen aiwatar da sabbin dokokin haraji, tana mai kafa hujja da wasu rashin tabbas kan matakan ƙarshe da aka bijiro da su cikin sabuwar dokar.

Shugaban Kwamitin Shugaban Ƙasa kan tsarin harajin, Taiwo Oyedele ne ya bayyana hakan yayin wata ganawa da manema labarai a birnin Legas, yana mai cewa akwai nazarce-nazarce da ya kamata a kammala bibiya kafin fara aiwatar da dokar.

Oyedele ya ce tuni ya shaida wa hukumomin da ke da ruwa da tsaki a ɓangaren haraji su dakata da duk wani aiki da ya shafi wannan doka.

Dokar haraji ta Najeriya, wadda ta fara aiki a ranar 1 ga Janairu, ta fuskanci suka bayan zargin cewa anyi sauye-sauye da majalisar dokokin ƙasar ta amince da su, akwai ɗungushe a ciki.

Sai dai Oyedele ya nuna damuwa kan yadda wannan mataki ke fuskantar caccaka, yana mai danganta hakan da yaɗa labaran ƙarya da nufin kawo cikas ga sabon tsarin harajin.

Ya ce yadda aka riƙa yamaɗiɗin labaran ƙarya a bara, hakan ya sanya Najeriya yin asarar Naira tiriliyan 4.6 a rana guda cikin watan Nuwamba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp