Home Labarai Shugaba Tinubu ya nada Jakadan da zai wakilci Nijeriya a Amurka

Shugaba Tinubu ya nada Jakadan da zai wakilci Nijeriya a Amurka

Shugaba Bola Tinubu ya amince da nadin jakadu hudu, daga cikin 68 da Majalisar Dattawa ta amince da su a watan Disamban 2025.Tinubu ya tabbatar da nadin Ayodele Oke a matsayin jakadan da aka nada a Faransa, da kuma Lateef Are a matsayin jakadan da aka nada a Amurka.

Shugaban Najeriya ya kuma tabbatar da nadin Amin Dalhatu, tsohon jakadan Korea ta Kudu, a matsayin babban kwamishina da aka nada a Birtaniya.

Usman Isa Dakingari Suleiman, tsohon gwamnan Kebbi, shi ne jakadan da aka nada a Turkiyya,ƙasar da Shugaba Tinubu zai fara ziyara a mako na sama.

A cikin wata sanarwa da ya aike wa Ma’aikatar Harkokin Waje, Shugaba Tinubu ya bukaci ma’aikatar ta sanar da gwamnatocin kasashen hudu game da nadin jakadun, bisa ga tsarin diflomasiyya.

Mai baiwa shugaba Tinubu shawara kan dabaru da hulda da manema labarai Bayo Onanuga,ya jaddada manufar shugaba Tinubu na ganin Najeriya ta shiga sahun manyan ƙasashe a fanin diflomasiyya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp