Mayaƙan Iswap sun kashe sojojin Najeriya a harin jirage marasa matuƙa

Rundunar tsaron Najeriya ta tabbatar da cewa mayaƙan Iswap sun kai hari kan sojojinta a garin Sabon Gari da ke jihar Borno a arewa maso gabashin ƙasar.

Rundunar ta ce an kai harin ne a ranar Alhamis ɗin da ta gabata, kuma ta ƙara da cewa mayaƙan sun yi amfani ne da jirage marasa matuƙa.

A sanarwar da rundunar tsaron ƙasar ta fitar, ta ce hare-haren sun yi sanadiyar mutuwar wasu sojoji da ba ta bayyana adadinsu ba.

Mai magana da yawun rundunar, Sani Uba, ya ce an kai harin ne a wani sansanin soji da ke yankin, amma ya ce, “sojojin sun daƙile harin, sannan komai ya lafa.”

A sanarwar da ya fitar a ranar Alhamis, Mr Uba ya ce kafin harin, sojojin na Najeriya sun kai hare-hare a yankin Bulo Dalo, inda a cewarsa suka kashe mayaƙa 12, sannan suka kai wani harin a garin Garno shi ma na jihar ta Borno duka a ranar Laraba, inda a cewarsa a can ma suka kashe mayaƙan guda shida. Ya ƙara da cewa sojojin sun ƙwace makamai da alburusai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com