Home Taska Matsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar Abuja

Matsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar Abuja

Protest Insecurity

Matsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar Abuja

 

A ranar Asabar, masu zanga-zanga sun tare gadar da ke kan hanyar Karu zuwa Nyanya, wacce ta haɗa Abuja da Jihar Nasarawa.

Masu zanga-zangar na neman a inganta tsaro saboda yawaitar sace-sacen mutane da hare-hare.

Sun riƙe kwalaye masu rubutu tare da rera waƙoƙi suna zanga-zanga, suna cewa gwamnati dole ta ƙara ƙaimi wajen kare rayuka da dukiyoyi.

Sun taru a kan gadar yankin, sannan daga baya suka yi tattaki zuwa Nyanya.

Wannan ya jawo cunkoson ababen hawa a kan hanyar Abuja zuwa Keffi, inda matafiya da dama suka maƙale na tsawon sa’o’i.

Masu zanga-zangar sun ce rayuwa ta yi wahala saboda rashin tsaro, kuma sun buƙaci gwamnati ta ɗauki matakan gaggawa.

An tura jami’an tsaro domin sanya ido da kuma kula da zirga-zirgar ababen hawa.

An kuma shawarci direbobi su bi wasu hanyoyi daban.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a samu rahoton tashin hankali ko raunuka ba, amma an tare hanyar lamarin da kawo tsaiko ga masu ababen hawa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Manyan Tsofaffin Jami'an Soji 10 da Suka Rasa Rayukansu a Hannun ƴan Ta'addaTarihin Rayuwar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaMatsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar AbujaDuk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da 'Yan Ta'adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda - Christopher MusaFarashin ɗanyen Mai ya Faɗi Bayan Amurka ta Soke Sabbin Hare-Haren kaiwa IranAmurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran - TrumpMajalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan JihaHukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar NejaMiyagun ƙwayoyi da Makamai: Jami'an Tsaro Sun Kama Mutane 8 a Jihar YobeAbin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto
X whatsapp