Home Taska Duk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da ‘Yan Ta’adda, za a ɗauke...

Duk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da ‘Yan Ta’adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda – Christopher Musa

Christopher-Musa

Duk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da ‘Yan Ta’adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda – Christopher Musa

Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya bayyana cewa ci gaba da matsalar ta’addanci da fashi da makami a ƙasar na faruwa ne saboda goyon bayan da ’yan ta’adda ke samu daga wasu ɗaiɗaikun mutane da ke ba su abinci, bayanan sirri da kuma kuɗaɗen shiga.

Ya bayyana haka ne wajen jawabin da ya gabatar a wajen babban taron ƙasa da aka gudanar a Jihar Legas.

Ministan ya jaddada cewa akwai mutanen da ake haɗa baki da su da kuma waɗanda ke ɗaukar nauyin ’yan ta’addan a cikin al’umma, waɗanda ya ce su ne ke ci gaba da rura wutar ta’addanci a Najeriya.

Ministan ya bayyana cewa jami’an tsaro na fuskantar ƙalubale wajen kai hare-hare saboda ’yan bindigar na fakewa a cikin fararen hula.

Janar Musa ya ƙara da cewa duk wanda aka kama yana taimaka wa ’yan ta’adda ko yin kasuwanci da su, za a ɗauke shi a matsayin ɗan ta’adda.

Ya buƙaci al’umma da su gaggauta fallasa masu haddasa rikici da masu tallafa musu domin kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta addabi ƙasar, musamman Arewacin Najeriya.

Tsohon Janar ɗin sojin ya gargaɗi gwamnonin jihohi da su daina yin sulhu da ’yan ta’adda, yana mai cewa hakan ba mafita ba ce, face dabarar da ’yan bindigar ke amfani da ita wajen sake shirya kansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dr Lawan Sani: Yadda Masanin Tsaron Intanet Ya Zama Sarkin Gumel: Daga Shuaib S. AgakaAllah ne Kawai Zai Iya Hana Tinubu Cin Nasara a 2027 — Datti"Dangantakar Farar Hula da Sojoji Itace Mabuɗi ga Tsaron Ƙasa da Shugabanci Nagari" — Tsohon CDS IraborRundunar Sojin Najeriya ta Binciki Zargin Cin Zarafin Jima'i da Aka yi wa Kyaftin a JosBabban Jami’in EFCC na Fuskantar Zarge-Zargen Cin Hanci da Dukiyar da ba a San Asalinta baƳan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan Gaba
X whatsapp