Home Taska Duk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da ‘Yan Ta’adda, za a ɗauke...

Duk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da ‘Yan Ta’adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda – Christopher Musa

Christopher-Musa

Duk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da ‘Yan Ta’adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda – Christopher Musa

Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya bayyana cewa ci gaba da matsalar ta’addanci da fashi da makami a ƙasar na faruwa ne saboda goyon bayan da ’yan ta’adda ke samu daga wasu ɗaiɗaikun mutane da ke ba su abinci, bayanan sirri da kuma kuɗaɗen shiga.

Ya bayyana haka ne wajen jawabin da ya gabatar a wajen babban taron ƙasa da aka gudanar a Jihar Legas.

Ministan ya jaddada cewa akwai mutanen da ake haɗa baki da su da kuma waɗanda ke ɗaukar nauyin ’yan ta’addan a cikin al’umma, waɗanda ya ce su ne ke ci gaba da rura wutar ta’addanci a Najeriya.

Ministan ya bayyana cewa jami’an tsaro na fuskantar ƙalubale wajen kai hare-hare saboda ’yan bindigar na fakewa a cikin fararen hula.

Janar Musa ya ƙara da cewa duk wanda aka kama yana taimaka wa ’yan ta’adda ko yin kasuwanci da su, za a ɗauke shi a matsayin ɗan ta’adda.

Ya buƙaci al’umma da su gaggauta fallasa masu haddasa rikici da masu tallafa musu domin kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta addabi ƙasar, musamman Arewacin Najeriya.

Tsohon Janar ɗin sojin ya gargaɗi gwamnonin jihohi da su daina yin sulhu da ’yan ta’adda, yana mai cewa hakan ba mafita ba ce, face dabarar da ’yan bindigar ke amfani da ita wajen sake shirya kansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INECJam'iyyar NDC ta Buƙaci Sanata Hanga da Gaya da su Sake Tunani Kan Sauya SheƙaYan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi Mataimakinsa
X whatsapp