Home Taska Duk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da ‘Yan Ta’adda, za a ɗauke...

Duk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da ‘Yan Ta’adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda – Christopher Musa

Christopher-Musa

Duk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da ‘Yan Ta’adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda – Christopher Musa

Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya bayyana cewa ci gaba da matsalar ta’addanci da fashi da makami a ƙasar na faruwa ne saboda goyon bayan da ’yan ta’adda ke samu daga wasu ɗaiɗaikun mutane da ke ba su abinci, bayanan sirri da kuma kuɗaɗen shiga.

Ya bayyana haka ne wajen jawabin da ya gabatar a wajen babban taron ƙasa da aka gudanar a Jihar Legas.

Ministan ya jaddada cewa akwai mutanen da ake haɗa baki da su da kuma waɗanda ke ɗaukar nauyin ’yan ta’addan a cikin al’umma, waɗanda ya ce su ne ke ci gaba da rura wutar ta’addanci a Najeriya.

Ministan ya bayyana cewa jami’an tsaro na fuskantar ƙalubale wajen kai hare-hare saboda ’yan bindigar na fakewa a cikin fararen hula.

Janar Musa ya ƙara da cewa duk wanda aka kama yana taimaka wa ’yan ta’adda ko yin kasuwanci da su, za a ɗauke shi a matsayin ɗan ta’adda.

Ya buƙaci al’umma da su gaggauta fallasa masu haddasa rikici da masu tallafa musu domin kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta addabi ƙasar, musamman Arewacin Najeriya.

Tsohon Janar ɗin sojin ya gargaɗi gwamnonin jihohi da su daina yin sulhu da ’yan ta’adda, yana mai cewa hakan ba mafita ba ce, face dabarar da ’yan bindigar ke amfani da ita wajen sake shirya kansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga Legas
X whatsapp