Home Labarai Majalisar Wakilan Nijeriya ta Zargi NNPC Da Badakalar Dala Biliyan 10 Na...

Majalisar Wakilan Nijeriya ta Zargi NNPC Da Badakalar Dala Biliyan 10 Na Tallafin Man Fetur

Majalisar wakilan Nijeriya ta yi zargin cewa an sace sama da Dalar Amurka Biliyan 10 na danyen man fetur, ta hanyar badakalar tallafin Man wanda kamfanin man fetur na kasar NNPC da sauran masu ruwa da tsaki a kamfanin su ka yi.

Don haka majalisar ta kafa wani kwamitin wucin gadi da zai binciki tsarin tallafin man fetur tsakanin shekarar 2017 zuwa 2021 da ga kamfanin na NNPC ya yi.

Hakan ya biyo bayan amincewa da kudirin da Dan majalisa mai wakiltar Edo Sergious Ogun ya shigar gaban majalisar a ranar laraba a birnin tarayya Abuja.

Ta cikin kudirin nasa, Mista Ogun yace an sanar da shi cewa a shekarar 2002, kamfanin na NNPC ya sayi danyen mai a farashin kasuwannin duniya, wanda ya kai ganga 445,000 a ko wacce rana.

Ya kara da cewa anyi hakan ne domin bada damar samar da man da ake amfani da shi a cikin gida, amma abin damuwar shine yadda a shekarar 2002 matatun man Nijeriya ke samar da ganga 445,000 a kowacce rana.

Sai dai kuma yace daga bisani karfin matatun ya ragu zuwa sifili sakamakon rashin inganci da kuma zargin cin hanci da rashawa ga masu ruwa da tsaki ya durkusar da fannin.

By PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp