Gwamnatin Jihar Kano zata Kaddamar da Sabuwar Tashar wutar Lantarki a jihar

Gwamnatin Jihar Kano a Arewacin Najeriya ta ce nan da makwanni 6 za a kammala aikin tashar samar da wutar lantarki ta Tiga mai karfin mega watt 10
Gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje ya ba da tabbacin ne lokacin ziyarar ganin yadda aikin tashar samar da wutar lantarki na Tiga da na samar da ruwa da ke Tamburawa yake gudana.
Cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran gwamnan Malam Abba Anwar ya fitar a jihar Kano, ta ce tashar samar da wutar lantarkin a matakin gwaji kafin kaddamarwa.
Gwamnan ya kuma yabawa kamfanin samar da hasken wutar lantarki mallakin jihar KHEDCO da kamfanin da aka baiwa kwangilar aiki da kuma sauran masu ruwa da tsaki.
A cewar gwamnan na da makwanni kadan wutar lantarkin na Tiga za a jona shi da tashar samar da ruwa ta Tamburawa , yana mai bada tabbacin cewa zai yi iyakar kokari dan ganin ya bar tarihi a dukkanin bangarorin ciyar da al’umma gaba.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 30 minutes 1 second,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 11 minutes 26 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com