Home DUNIYA Wani sabon hari a Jamhuriyyar damukradiyya congo yayi sandiyyar mutuwar mutane 40

Wani sabon hari a Jamhuriyyar damukradiyya congo yayi sandiyyar mutuwar mutane 40

Wani sabon harin mayakan tayar da kayar baya na ADF a gabashin jamhuriyyar damukradiyyar Congo yayi sanadiyyar mutuwar mutane 40 kamar yadda hukumomi suka bayyana.

Shugaban wata kungiyar Al’umma a kauyen mukondi ne ya tabbata da faruwar lamarin inda yace  mayakan sun hallaka mutanen ne da wukake.

Kungiyar ‘yan tawayen ADF ta samo asali ne daga kasar Uganda wadda ta fara gudanar da ayyukan ta a gabashin Congo a tsakiyar shekarun 1990, wanda aka ce mafi yawa cikin ‘ya’yan kungiyar musulmai ne dake kisan gilla ga fararen hula.

A  shekara 2021 ma an alakanta hare-hare da aka kai kasar Uganda kuma aka kaddamar da wani farmaki na hadin gwiwa tsakanin sojojin congo da na Uganda domin farautar mayakan a Arewacin Kivu da kuma lardin Ituri dake makwabtaka da su.

Ko a makon daya gaba ta kasar Amurka ta sanya tukuicin dala miliyan biyar ga wanda ya bayar da bayanan yadda za’a kama shuganban kungiyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp