Home DUNIYA Wani sabon hari a Jamhuriyyar damukradiyya congo yayi sandiyyar mutuwar mutane 40

Wani sabon hari a Jamhuriyyar damukradiyya congo yayi sandiyyar mutuwar mutane 40

Wani sabon harin mayakan tayar da kayar baya na ADF a gabashin jamhuriyyar damukradiyyar Congo yayi sanadiyyar mutuwar mutane 40 kamar yadda hukumomi suka bayyana.

Shugaban wata kungiyar Al’umma a kauyen mukondi ne ya tabbata da faruwar lamarin inda yace  mayakan sun hallaka mutanen ne da wukake.

Kungiyar ‘yan tawayen ADF ta samo asali ne daga kasar Uganda wadda ta fara gudanar da ayyukan ta a gabashin Congo a tsakiyar shekarun 1990, wanda aka ce mafi yawa cikin ‘ya’yan kungiyar musulmai ne dake kisan gilla ga fararen hula.

A  shekara 2021 ma an alakanta hare-hare da aka kai kasar Uganda kuma aka kaddamar da wani farmaki na hadin gwiwa tsakanin sojojin congo da na Uganda domin farautar mayakan a Arewacin Kivu da kuma lardin Ituri dake makwabtaka da su.

Ko a makon daya gaba ta kasar Amurka ta sanya tukuicin dala miliyan biyar ga wanda ya bayar da bayanan yadda za’a kama shuganban kungiyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp